LABARAN MAKO
GABATARWA Salamu alaikum barkanmu da sake saduwa a wannan shafi namu mai kawo muku labarai, da al'amura na yau da kullum, wato nishadisport nine naku Sadik Yusuf har kullum da fatan kuna lafiya. Kwamishina ya aje mukaminsa Ga sharhin labaran dallah-dallah. Kwamishinan sufiri na jihar kano Ibrahim Namadi, ya ajiye mukaminsa na kwamishina bisa radin kansa acewarsa.inda yake cewa: "na aje mikamina na kwamishinan sufiri, saboda na kare kima, da martabar Gwamnatin jiha kar kashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf, saboda abin da yafaru dan gane da belin wanda ake tuhuma da aikata lefin safarar miyagun kwayoyi. "hakan ta farune saboda banyi cikakken bincikeba, na karbe shi saboda haka na ga ya dace da nayi murabus, kuma na bawa al'ummar jihar kano hakuri da gwammnati, da yan jam"iya bisa abinda yafaru." "Ina mika godiyata ga gwamna, saboda damar da yabani ta hidimtawa al'ummar jihar kano na gode." Kuma ya kara da cewa "na yi farinciki ...