Posts

DUKAN DUHU- KASHI NA 3

  GABATARWA Salamu alaikum masoya wannan dandali namu, na nishadisport. Wanda muke kawo muku dadadan labarai, na kasa, da kuma labarin fina-finai wanda muke juyasu izuwa bidiyo, a manhajar youtube mai suna ( nishadisport). Daga Sadik Yusuf, wanda shine yake kokarin yi muku, wannan ✍️ rubutu da fatan kuna gamsuwa, na gode!. Ga cigaban labarin Dukan Duhu na 3  SALE DAURE A WANI KANGO  Bayan yaran alhaji sun kamo Sale, sun daure shi a cikin wani gini wanda ba'a karasaba, yana daure bai san inda kansa yakeba. Kawai sai suka zuba masa ruwa, ya farka firgigit. Sai yaga alhaji tsaye da yaransa sun hada rai kamar saci babu, sai alhaji ya kece da dariya irin ta mugunta, ya kalli Sale yai shiru bai ce komaiba. Sale ya kallesu daya bayan daya ya sunkuyar da kansa kasa, Alhaji ya zuba masa na mujiya, sai ya kada baki yace: Alhaji:  "Malam Salele mai liki,  yanzu gaka a hannuna, naima tayin kudi, kaki karba. Kace ko za'a tsireka jininka ya dige kasa, bazaka sayarmana da soya...

DUKAN DUHU KASHI NA 2

DUKAN DUHU KASHI NA BIYU  GABATARWA Salamu alaikum masoya wannan dandali namu, wanda muke kawomuku dadadan labarai masu cike da darasi, waɗanda suke taba zamantakewar rayuwar mu ta yau da kullum. Zamu ci gaba da kawo muku cigaban labarin "DUKAN DUHU KASHI NA BIYU" . Sai ku biyo mu a hankali don jin yadda zata kaya. Ni ne naku Sadik Yusuf , na gode! SAILUBA TAJE WAJEN KAWARTA NEMAN SHAWARA Sailuba tana ba kawarta labarin yadda sukai da Alhaji. Ita dai Halima ta tsaya tana sauraronta, tayi zugum da ido. Halima tace: "Nidai abinda zan gayamiki Sailuba, ki nutsu ki tsaya wajen talakanki, domin shi yafi dacewa da ke. Kar ki jifan gafiyar baidu." Sailuba ta harareta cikin mamaki, tace: "Yau kuma kece mai fadin haka? Ke da nake zato zaki maramin baya, amma sai naji wata banzar magana ta futo daga gareki haka." Halima ta kara cewa: "To ai gaskiya ne. Abinda yasa kika ga ina kin sale, saboda naga ba’a sa muku rana ba, kuma ba’a yi baikon ba. Tu...

A CHUCI MATA kashi na biyu

Image
    GABATARWA  Salamu alaikum masoya wannan dandali namu wato nishadisport. Muke muku barka da wannan lokaci zamu cigaba da kawomuku labarin "A chuchi Mata" kashi na biyu, wanda yake kirkirarren labarine ba da kowa akeba. Da fatan za ku biyomu kuga yanda zata kaya.                               Hoton faster Achuci mata  FATIMA NA BA UMMAN TA LABARI TSAKANINTA DA SAURAYINTA  Fatima ta isa gida ta shaidawa babarta abinda ya gudana tsakanin ta da saurayin da ta yiwa tsiya, tqi watsi da shi.  umman tata tace: "Ai haka yafi, yaje ya karata matsiyaci kawai." Suka tafa da maman tata suna shewa.   Boss yazo gun Fatima Boss me badda kama, yazo ya tabbatar wa da Fati cewa auranta  zaiyi, ta amince dashi, sukai sallama ya tafi, itama ta shiga gida ta gayawa ummanta yanda sukai. Fati tace: "wannan mutumin da yazo wai cewa yayi zai aureni".sai  Umman tata:tace " haka yace?....

A chuci Mata-kashi na 1

Image
    Salamu alaikum masoya wannan dandali namu naku mai farinjini wanda kuke son ji da gani da karatu ku biyomu a NishadiSport – A Chuci Mata (Kashi Na Daya) Rubutawa: Sadik Yusuf         Gabatarwa  Assalamu alaikum masu bibiyar tashar NishadiSport, ni ne naku Sadik Yusuf. Muna kawo muku dadadan labarai, da fatan kuna jin dadin shirye-shiryenmu. wannan labari na "Achuci Mata" kirkirarren labarine anyishi ne badan waniba ko kuma wata , kawai dai labarine,kada wani yaga wani abu da yai kama da halinsa ya zaci dashi muke mun gode!.🙏 * RIGIMA BOSS DA ISAH A wani gari, akwai wasu abokai suna rigima akan wani bashi da Isah yake bin abokinsa mai suna Boss. Isah ya rike wuyan Boss suna kokawa yana cewa sai an biyashi kudinsa da ya kai shekara guda ba'a biyaba.  Suka cukume suna kokawa a tsakaninsu titi-titi   Boss ya samu sa’a ya daga Isah ya bugashi da kasa har ya ji masa rauni, sannan ya gudu ya barshi a nan yana murkususu. Da kyar Isah y...

Rikicin daba a kano

     GABATARWA Rikicin ‘Yan Daba a Kano, a ga ya za'a kamo bakin zaran.Daga Sadik Yusuf, Kano Nigeria Zami duba da wannan matsala da kuma wasu al'amura na yau da kullum. Dafatan za'a kasance damu. Daga Sadik Yusuf – Kano, Nigeria Tuntuba: sadiku854@gmail.com Shafinmu: nishadisport.blogspot.com Abin Da Ke Faruwa a Kano Ya kamata mu fuskanci abinda ke faruwa mu fadawa kanmu gaskiya, game da matsalar da ke addabar jihar Kano – wato rikicin 'yan daba.  Wannan matsala da take nema ta gagari Kundila  ta shafi unguwanni da dama a jihar ta kano , kamar irinsu  Dorayi, Sheka, Dala, Zage, Kofar Mata  s harada, ja'in da kuma kurnar Asabe  da dai sauran su. A bin yazama kamar annoba.Yara da basu kai shekaru 15 zuwa 18 ba suna haduwa suyi gungu suna fada a da makamai a  tsakaninsu,  suna kai hare-hare a inda suke so.  Suna amfani da makamai masu hadari irin su adda, barandami, fafalo , da kuma kayan maye da suke shaye-shaye. Sau da dama. ...

LABARAN MAKO

Image
  GABATARWA  Salamu alaikum barkanmu da sake saduwa a wannan shafi namu mai kawo muku labarai, da al'amura na yau da kullum, wato nishadisport nine naku Sadik Yusuf har kullum da  fatan kuna lafiya. Kwamishina ya aje mukaminsa  Ga sharhin labaran dallah-dallah. Kwamishinan sufiri na jihar kano Ibrahim Namadi, ya ajiye mukaminsa na kwamishina bisa radin kansa acewarsa.inda yake cewa:  "na aje mikamina na kwamishinan sufiri, saboda na kare kima, da martabar Gwamnatin jiha kar kashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf, saboda abin da yafaru dan gane da belin wanda ake tuhuma da aikata lefin safarar miyagun kwayoyi.  "hakan ta farune saboda banyi cikakken bincikeba, na karbe shi saboda haka na ga ya dace da nayi murabus, kuma na bawa al'ummar jihar kano hakuri  da gwammnati, da yan jam"iya bisa abinda yafaru."  "Ina mika godiyata ga gwamna, saboda damar da yabani ta hidimtawa al'ummar jihar kano na gode." Kuma ya kara da cewa "na yi farinciki ...

DUKAN DUHU- NA DAYA

   GABATARWA   Salam yan uwa masu bin wannan shafi namu na blogs, wato nishadisport munamuku maraba da sake saduwa, nine naku Sadik Yusuf,   ga sharhin shirin " Dukan Duhu." Bayanin shirin Wannan labari da akawa lakabi da " Dukan Duhu"  labarine da yake nuna cewa kada mace ta juya baya, bayan angama komai na sha'anin aure. Saboda hakan ya haramta inko aka aikata haka to sai a saurari abinda zaije yazo. Kamar dai yadda aka musalta a wannan labari, kuma labarin ba da wani akeba, madallah. A gidan su Sailuba Suna magana da Babanta da mamanta. Umma tana magana tace:  "Wai, ni, baban Sailuba, mai katanada dangane da bikin wannan yarinya Sailuba."  Baban Sailuba yace: "To,! Amma dai kinfi kowa sanin halin da na tsinci kaina a yanzu ya kike so nayi, sata ko fashi" ta tari numfashinsa. Umma: "To,! duka, kaje kayi mana, ni dai kawai a wuyanka nake neman Gado da Kawaba ehe!" Nan ya yanke jiki ya fadi kasa tum, yasamu shanyewar barin jiki dama...