A chuci Mata-kashi na 1

   Salamu alaikum masoya wannan dandali namu naku mai farinjini wanda kuke son ji da gani da karatu ku biyomu a

NishadiSport – A Chuci Mata (Kashi Na Daya)

Rubutawa: Sadik Yusuf

        Gabatarwa 

Assalamu alaikum masu bibiyar tashar NishadiSport, ni ne naku Sadik Yusuf. Muna kawo muku dadadan labarai, da fatan kuna jin dadin shirye-shiryenmu.

wannan labari na "Achuci Mata" kirkirarren labarine anyishi ne badan waniba ko kuma wata , kawai dai labarine,kada wani yaga wani abu da yai kama da halinsa ya zaci dashi muke mun gode!.🙏



* RIGIMA BOSS DA ISAH

A wani gari, akwai wasu abokai suna rigima akan wani bashi da Isah yake bin abokinsa mai suna Boss. Isah ya rike wuyan Boss suna kokawa yana cewa sai an biyashi kudinsa da ya kai shekara guda ba'a biyaba. 

Suka cukume suna kokawa a tsakaninsu titi-titi  Boss ya samu sa’a ya daga Isah ya bugashi da kasa har ya ji masa rauni, sannan ya gudu ya barshi a nan yana murkususu. Da kyar Isah ya mike, ya tafi gida yana dafe kai.

Boss ya fada wa abokinsa Musa abin da ya faru, sai Musa yace:

“Ahh! Boss, baka kyauta ba. Yaya za’a yi mutum yana  binka bashi har shekara guda ka ki biyansa,don yaui magana ka kamashi rigima. kuma ka ji masa rauni. Wannan rashin imani ne.”

Boss ya ce:

“Kai tsiyata daman daman da kai, haka kake . Kullum sai ka ce za ka fada wa mutum gaskiya wai kai ga  na Allah mai san zaman lafiya.”

Musa ya amsa:

“Ni ba abinda zai hanani fadar gaskiya, komai dacin ta. Idan baka son gaskiya  ka daina zuwa gurina, sai dai ka daina — amma gaskiya sai na  fada ma ita.”

Boss ya ce:

“To shikenan, ka yi kar ka fasa. Ni kuma ba zan canza ba sai naga yadda zakayi, kawai dan yana bina bashi sai ya cimin zarafi wallahi bazata yowuba.”

Sai ya tashi ya tafi ya bar Musa yana ban-bami.


* ISAH YA SHIGA GIDA

gida kuwa, Isah yana shigowa yana dafe kai sai kanwarsa Fati ta fito tana shirin zuwa kanti. Ta gan shi yana dingishi, ta tambaye shi abin da ya faru.

Isah yace:

“Wallahi Boss ne ya min wannan wulakancin akan bashi da nake binsa bashin kuma har na tsawon shekara guda.” tana kallon sa tana jimami. Sai,

Fati tace:

“Wannan mutumin fa mugune kainema kake zuwa gunsa yakamata ka chanza guri domin ba tsararka bane shi mutumin banzane.” yana dafe kai yana nishi ya shige gida ita kuma ta fita.


Washe gari Boss da Musa suna zaune, sai Boss ya hango wata yarinya tana tafiya.

Boss ya ce:

“Kai Musa, haka wannan yarinyar ta zama!”

Musa ya ce:

“Wace yarinyar? Ai ba ka ganeta ba? Kanwar Isah cefa!”

Boss ya ce:

“ kai! Ban ganetaba itace ta zama haka.Wallahi ina sonta.”

Musa ya ce:

“To ka manta da komai da kayi musu kenan? Duk azabtarwar da kayi wa 'yan gidansu sata kwace. Kuma ka manta kwanannan me kaiwa yayanta?.”

Boss ya ce:

“Kai kawai ka goya min baya don na cimma burina malam sarkin gaskiya.”

Musa ya ce:

“Ni gaskiya zan fada, wannan yarinya tafi karfinka don kai ba mutumin kirkine ba ne, ko da kana so ko ba ka so sai na fada.” Boss yana kallonsa yayi kwafa, yatashi ya barshi.



* BOSS YA KWACEWA YARO KUDIA

 wani lokaci, wani yaro na kan hanya an turo shi da kudi, sai Boss ya tare shi ya kwace kudin. Yaron ya koma gida yana kuka, Fati ta tareshi shi. Ta tambayeshi waye?.

Ashe yaron shima kanin fatine wadda Boss ykecewa zai aura.

Yaron yace:

“Wannan mugun mutumin nanne Boss na gurinchan shine ya kwace min kudi.”

Fati tace:

"Wannan Boss din mara mutumci shine ya kwace mana kudin"?.

Suka tafi wajen domin fati ta karbo kudin a wajen Boss din, amma Boss yana hango su dai yatashi ya bar gun ya  gudu ya ɓuya. Suka duba basu ganshiba suka koma.



* SAURAYIN FATI YAZO

Saurayin Fati ya zo wajen ta, suna hira. Ya shaida mata cewa ya gama gina gidansa kuma ya shirya da gaske don aure.

Fati tace:

“Insha Allah zan tsaya akan alkawari. Ba zan yaudare ka ba, kar kaji komai nayi murna da jin wannan labari.”

Sai suka ci gaba da tattaunawa cikin farin ciki, sannan saurayin nata ya tafi.



* BOSS YA ARO KAYA 

Boss ya je ya aro kaya, ya gyara jikinsa, ya aro mota, ya je kofar gidan su Fati. Ya sha kamshi, yana takama da alamar alhaji ya aika aka kira fatima.

Fati ta fito, bata ganeshi ba.

Boss yace:

“Ni baƙone daga Dubai, nagan ki, ke kin kama zuciyata... Naga ina sonki matuka da gaske."

fati tace: "to a ina kasanni? ina ka taba ganina?kai da kace jiya kazo garinnan."

Boss:

"ah! Bakece kika zo wucewa ta kusa da kantin chanba? Dake da wani yaro, ai anan na ganki." Ita dai tana kallon sa alamar kamar ta ganeshi shi kuma yana boyewa.

Fati tace:

“Ni ina da wanda zan aura cikin sati guda,za'a daura mana aure don haka kayi hakuri kaga tafiyata.” A ki tsaya mana bamu gama maganaba.

Ta barshi a wurin yana girgiza kai.


* TA BA MAMANTA LABARI 

Ta shiga gida sai taba maman ta labarin yadda sukayi da wannan Boss din wai yana sonta sai maman tace:

"Waye kuma wannan a ina yake." Tana kallon Fati.

Fati:

"Wai cewa yayi bakone shi jiya yazo daga dubai domin kawo wasu kaya a kwantena." Maman tata tana jinjina lamarin. Sai ta tashi ta tafi ta cigaba da aikinta.


* BOSS DA ABOKINSA 

Boss ya samu abokinsa yana bashi labarin Fatima.

Boss:

"Ai inatinanin yarinyar zata amince dani, ga yadda naga tana dan satar kallona ta gefen ido."shi dai abokin nasa yana jin labarin banza.

Abokin yace:

"kai ka faye rigima yanzu ya zakai, randa akace ta ganeka? da shirmenka"

Boss yace:

"yo ba karamar kwakwalwa ce dasuba? haka zan jasu bazasu ganeba." 

Musa yace:

"Ai zamuyi kallo nan gaba zamu ga yadda za ai" inji shi.


* ISAH YAZO ZANCE 

Isa tsaye yana jiran Fatima da dan kekensa a hannu, keken ma turoshi yayi, sai da tagama bata masa lokaci kana ta futo.

Ta taho kamar mara lafiya tana sanda, sai isa ya kalleta cikin mamaki domin ba haka ya saba ganintaba, har dai ta karaso.

Isa yace:

"Lallai yau a kwai magana, na ganki ba kamar yadda muka sababa." Ta kalleshi a wani hargitse tana wani harare-harare, sai takada baki tace:

"Lallai a kwai magana kuwa me katanada game da inda zamu yawon shaka tawa bayan anyi biki?." Isa yai dam! Ya zura mata ido yarasa wannan wace irin tambayace.

Isa yace:

"Me kika ce" Fatima tace abinda kaji shi nake nufi." Ya dafa keya ya rasa me zai ce sai yace: "me kike nufi da wannan magana."

Fatima:

"Ina nufin irnsu Dubai, America, chana, da kuma irinsu saudiyya." Yai shiru yana kallonta jiki a sanyaye.

ta ci gaba da magana: "to in baka da abin fada ni kaga ta fiyata. Domin ni yamzu nayi chanji naga alama kai baka shiryaba". 

haka ta tafi ta barshi tsaye yana numfashi sama-sama ya bita da Kallo tana tafiya tana magana: 

"Yauwa in kaje gida ka turo a karbi wannan tar kacen kayan naka da basu wuce cikin cokaliba talaka kawai." har ta shige gida tana magan.

shima dai da kyar yasamu ya bar gun yatafi kafadu ba nauyi.

  Karshen kashi na Daya 

■ Nan muka kawo muku karshen kashi na daya, inda kukaji yanda ta kasance tsakanin Boss da isa akan bashi.

■ Kuma Boss ya fada soyayya da Fatima kanwar isa sai abiyomu a kashi na biyu aga ya zata kaya Karanta kuma:


     Darasin da yake ciki

■ Mata su dena ruwan ido akan soyayya su rika tsayawa a kan gaskiya.

■ Kuma mutum ya rika biyan bashi in ana binsa. Gashi daga bashi abin ya koma fada.



Nan ne muka kawo muku karshen kashi na daya na shirin A Chuci Mata. Ku kasance tare da mu don kashi na biyu.

Mun gode!🙏

Wanda ya rubuta: Sadik Yusuf
📧 Imel: sadiku854@gmail.com
📱 WhatsApp: 08148166212



 

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

DUKAN DUHU KASHI NA 2

An tarewa Sani hanya