Rikicin daba a kano
Mai gabatarwa sadik Yusuf Kano Nigeria,wato yakamata mu fadawa kanmu gaskiya dangane da abin da yake faruwa a Kano na rikicin Yan daba, da ya addabi wasu sassan unguwanni a jihar ta Kano,kamar irinsu,dorayi,sheka,dala,zage,kofar mata,da dai sauransu,saikaga yandaba Yara Wanda Basu gaza shekara sha biyar zuwa dha takwas ba sun hada gungu su tinkari duk inda suke so suyi ta fada ajunan su suna sure sare, wani lokacin ma har arasa rai suyi mummunan ta'adi Wani lokacin Harda kisan kai basa jin ko tsoron Allah balle ma huma wadda suke futo na fito da ita Suna jifan yansanda Wani lokacima suyi masu rauni ko kuma wanda baijiba bai ganiba asare shi ko asoka masa wuka inda karar kwana ya mutu, da mamaki inkaga makaman da suke yawo dasu abin Sai ya firgitaka irinsu adda,barandami,fafalo,ga kayan shaye shaye iri iri wanda ake ganin sune kanwa uwar gami wajen tunzurasu ,ba tausayi ba imani ba kunya ba tsoro, Allah ya kawo karshen wannan lamari.
To amma masana harkokin yau da kullum masu fashin baki, Suna ganin cewa ya kamata, iyaye anasu bangaren, sudena daurewa ya'yansu gindi, in sun aikata lefi irin wannan na daba da shaye shaye, ita kuma hukuma anata bangaren tarika yin hukunci basani ba sabo in akai hakan aji saukin lamarin,ita kuma gwammnati tasa Ido wajen hukunta masu laifi kada arika sakinsu domin ana zargin yansiyasa da karbar irin wa yannan bata garin daga hannun alkalai arika yin adalci a shariu ko asamu saukin lamura, amma abin nema yake ya gagari kundila ,don wasu unguwanni har gida suke shiga su karya kofa domin satar waya ko Ina suke kai wayar da baza'a kamasuba oho, to kowa yatashi ya farka yasa Ido yayi addu'ar samun Zaman lafiya da tsaro ko Al amura sa inganta saboda abin yayi yawa damai mutane zasuji Allah ya kyauta Amin summa amin.
Kuma ana bawa gwamnatin jihar Kano shawara kan ta lalubo hanyoyin magance wannan mataala tun daga tushe. Kamar samaria aiyukan yi ga matasa da bada ilimi mai inganci , da koya sanar hannu don dogaro da kai hakan zai taimaka matuka wajen samun saukin lamarin,kuma arika zuwa kowace unguwa lungu da sako masu wannan matsala a temakamusu ,ko kukuma ta hanyar tara samarinnan don ayimusu sulhu ,don azamin gwammnatin Rabi'u Musa Kwamkwaso anyi wani irin hobbasa wajen yin sulhu tsakanin unguwanni ta hanyar manyan kauraye irin na da saboda su wa yannan yara suna jin maganarsu ,aka ko samu saukin lamura.To mai zaihana itama wannan gwammnatin ta Alhaji Abba Kabir Yusuf ta dauki wanchan salon ko asamu dacewa muna fatan haka. Domin abin sai anhada hannu an hada karfi da karfe gwammnati da jama'ar gari saboda yaran suna bukatar ayi taron dangi akansu domin sunyi nisa basa jin kira .
Kuma ga wata matsala itama da ta kunno kai yanda yan adai daita sahu suke tasu tsiyar,su hadu su rika cutar mutane sunayi musu sata ta kaya ko ta waya ,daka shiga ciki sai suyima dabara in sunga sun yima sata sai suce sunyi mantuwa ba hanyar zasu biba, sao su saukeka su chanza hanya ,kai kuma kawai sai ka ga anyima sata musamman wayar salula itace tafi saukin sata .
Masu sharhi kan al'amuran yau da kullum suna cewa, yakamata anata bangaren gwammnati ta tashi tsaye wajan maganin wannan ga garumar matsala, gwammnati tayi hobbasa ta hana aiki na adai daita sahu daga karfe goma na dare zuwa karfe shida na yamma, hakan yasa aka dan sami saukin lamarin, amma har yanzu matsalar nacigaba da kankama.
Daga sadik yusuf A tuntubemu ta nan sadiku854@gmail.com
http//: nishadisport.blogspot.com
Comments
Post a Comment