Nigeria a yau

GABATARWA
 Salamu alaikum masoya wannan dandali namu wanada muke kawo muku labarai da al'amura na yau da kullum da zaman takewar al’umma, nine naku Sadik Yusuf nake kawomuku labaran.

 YAN WASAN DA SUKA WAKILCI JIHAR KANO SUNA HANYAR DAWOWA DAGA ENUGU,  SUN GAMU HADARIN MOTAR DA YA YI SANADIYAR MUTUWAR MUTANE 22

Yan wasan da suka wakilci jihar Kano, a wani wasan da aka fafata a jihar Enugu, yayin dawowarsu gida sun gamu da hadarin mota.


● Mutum ashirin da biyu sun mutu

 Wannan mummunan hadari ya yi sanadin mutuwar mutane 22, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata. Ciki harda masu horaswa,da 'yan wasa, drebobi, da sauransu.

 Jama’a da dama da suka jikkata suna karbar magani a asibiti inda ake basu kulawa ta musamman. Wadanda suka rasa rayukansu kuma, an yi jana'izarsu kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.

 Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini tare da jajantawa iyalan mamatan, da daukacin al’ummar Kano. Haka zalika, ya sha alwashin daukar nauyin kula da lafiyar wadanda suka jikkata tare da fatan Allah ya kare afkuwar irin haka a gaba.

Amma gwamnatin Kano tayi abin yabawa, domin ta kai daukin gaggawa inda abin ya faru. Nan akafara bawa wanda suka jikkata kulawar gaggawa, bisa jagorancin kwamishinan wasanni na jihar kano Mustafa Rabi'u Musa.


  Mustafa Rabi'u Musa  kwamishinan wasanni na kano. 


● Fadar shugaban kasa ta aike da sakon ta’aziyya 

 fadar shugaban kasa ta aike da sakon ta’aziyya, ga gwamnatin Kano da daukacin al’ummar Najeriya. Muna rokon Allah Madaukaki ya gafarta wa wadanda suka rasu, ya kuma ba wanda suka jikkata lafiya, ya hana faruwar makamancin hakan nan gaba.


SHARHI 

Yanada kyau gwamnati ta kula da abubuwan da suke haddasa hadura a kan titunan Nigeria.  Musamman manyan hanyoyi, saboda kullum xakaji ance anyi hadari a chan, ache anyi hadari a nan, kuma asamu rasa rai da kuma muna nan raunuka harda rasa dukiya baki daya.

Wannan lamari ya rataya kan hukuma, itace ke da alhakin lura da hanya da kuma lodin da masu mota keyi. Na ganganci. A kan tituna manya da kanana.

● Drebobi 

Sukuma masu motoci, drebobi manya dana kanan motoci, suma su kula da hakkin hanya su daina gudun wuce sa'a su dena lodin da ya wuce kima,  domin kowace mota akwai adadin abin da zata dauka, doramusu kaya dayawa yana sabbaba hadari.

 Sai kaga har a but din mota wajen zuba kaya, amma mutane ake turawa,har wajen zaman dreba mutane ake zubawa, don Allah mu gyara ko asamu sauki.



GAME DA CIN ZARAFIN DABBOBI – MU KULA DA HAKKINSU

A halin yanzu ana ta hada-hadar jigilar dabbobi daga gari zuwa gari, amma abin takaici shi ne yadda wasu ke nuna rashin tausayi da imani wajen mu'amala da dabbobin.

 Wasu mutane kan daure dabbobi a kafafunsu, su zauna a kansu a kan babur ko mota, suna tuka su ba tare da jin tausayinsu ba.

Wasu kuma su sasu amota a daure suyi tafiya mai nisa dasu. kasa-kasa gari ya gari ba maganar cin abinci bare kuma ruwa, haka zasu isa a galabaice, wasu kuma su rasa ransu a hanya. 

Idan ankaisu inda ake bukata sai kaga wasu basa iya tafiya sai sun huta, wasu ma sai sunkwana sun wuni kana zasu iya tashi, wasu kuma sai dai a yanka anan. Don haka jama'a sai mu gyara domin itama dabba tana da nata hakki akanmu.

Tambayar anan ita ce: Ina hukuma mai kare hakkin dabbobi take? Idan kuwa akwai, lokaci ya yi da za ta tashi tsaye wajen ganin an sauke nauyin da ya rataya a kanta.


 ● Gwamnati ta kafa hukumar kula da dabbobi.

Akwai bukatar gwamnati ta kafa dokar da ke kare hakkin dabbobi, ko ta farfado da ita idan tana nan. Dabbobi, koda ba mutane ba ne, suna da hakkin kulawa da tausayi kamar yadda addinin Musulunci da sauran kasashen duniya ke koyarwa.

A wasu kasashen waje, cin zarafin dabba yana iya kai mutum gidan yari. Amma a nan gida Nigeria, za ka ga yara ko manya na dukar dabba da igiya, har dabbar ta jikkata ko ta mutu. Ba mai cewa komai, ai wannan zalunci ne kuma Allah ba ya son zalunci.

Musulunci ya koyar da cewa in za ka yanka dabba, sai ka wasa wukarka sosai domin kar dabbar ta sha wahala. Ka kuma juya dabbar da fuskarta kasa, kada a nuna mata cewa za a yanka ta. Wannan koyarwa tana nuna muhimmancin jin kai ga halittu.ciki harda tsintsaye.

Don haka ina kira da kakkausar murya ga jama'a da su kiyaye hakkin dabbobi. Mu dinga nuna tausayi da jin kai, domin rayuwa da albarka tana biyo bayan aikata adalci.

 Allah yana son masu adalci, kuma duk abin da mutum ya shuka, shi zai girba.


MU SAUKAKAWA KANMU

Wato na lura da cewa ansamu saukin abubuwa na kayayyaki sun sauka, musamman ma kayan abinci,irinsu Wake,Dawa,Sahinkafa, Masara,Waken suya,da sauransu wannan abubuwa da na lissafa duk sunyi sauki a kasuwa.

Amma abin takaici, sai kaga masu saida abincin sayarwa basu kara hannuba, sunci gaba da sayarwa yanda suka saba. 

Don haka yakamata mutane muma muzama masu jinkai, ya sauko mu sauke in ya tashi mukara, wannan shine adalci,don kowa yasan cewa muma muna son juna. 

Amma in shugabanni sukayi ba dai-dai ba sai muyi cha akansu zagi  da suka,kuma muma bama wa kanmu adalci don Allah mu gyara.

gyara kayanka bai zama sauke muraba. Inkai sauki nima nayi sauki wanchanma yayi sauki, sai kaga kowa yasamu.


Ekpan an yanke masa daurin shekara shida

Kotu ta yanke wa Simon Ekpa daurin shekara shida a gidan gyaran hali na kasar Finland, saboda kotun ta sameshi da laifin zuga mutane su rika kai hare-hare ga mutanen da basu jiba ba su gamima.

Wai da zummar ballewa daga Nigeria, don kafa kasar Biafra, haka kuma ansame shi da karya doka da kuma zamba cikin aminci wanda hakan ya sabawa doka.

 ● Kotu ta kamashi da laifi

Kotu ta tuhumeshi da laifin aikata ta'addanci, ta hanyar zuga mutane su dau makamai da nufin kafa kasar Biafra, wanda kuma gwammnati ta haramta hakan.

Mutimin yayi wannan al'amari ne a shekarar 2021 zuwa watan nuwamba 2024 inda ya ingiza mutanensa a kudancin Nigeria, inda suke aikata laifukan da suka sabawa doka.

Kuma shine ya samar musu da makamai da abubuwan fashewa da harsa sai, suke aikata laifuka dasu.

Kuma yayi wannan laifuka ne a kasar ta Finland, kuma hakan ya sabawa doka,wannan hukunci da aka yanke, ba shibane na karshe, yana da, damar daukaka kara.

Wanda dama, tun a farko ya musanta zargin, da ake masa Allah ya sawaka.bbchausa  



KARSHEN NASIHA

Kowa ya kyautata — domin kowa zai ga alherin da ya aikata. 

Kowa yayi da kyau zaiga da kyau, Wannan shi ne sakona na yau. 

Kada ku manta ku dinga binmu a dandalinmu na NishadiSport, ku yi Subscribe, ku rika Sharing da Commenting. Muna godiya da kasancewa tare da mu.


Naku cikin girmamawa,

Sadik Yusuf

imel

๐Ÿ“ž08148166212





Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

A chuci Mata-kashi na 1

DUKAN DUHU KASHI NA 2

An tarewa Sani hanya