YAR MALAM SEASON 1 EPISODE 1 review

    Salamu alaikum barkanmu da  saduwa, a wannan  dandali namu wato nishadisport wanda muke kawo muku sharhin Shirin film din  'Yar Malam". Daga sadik Yusuf. 

 Shirin Yar Malam Kashi na daya, shirine  da yake nuna rashin  rike  amana  na wani mutum da dan uwansa ya mutu  ya  bar masa dukiya.

kamar  irinsu   gonaki, dabbobi,   da  kuma kudi,  da  gidaje ,  kuma  mutimin   mai  suna  M Nomau,  mutumin  kirkine  ya  temaki  dan uwan nasa ,mai suna Malam Idi.

 Amma  yaci  amanarsa  ya kasa rike wannan amana da yabashi. Sanoda rudin zuciya Ga kadan  daga cikin  episode one.  

  Sharhin kashi na daya.

 Ladidi na zaune a kusa da mahaifiyarta ta tashi don ta kaiwa babanta ruwa sai tasameshi a kwance ya kasa tashi, yana nishi sama-sama. 

Sai nan danan ta durkusa gabansa tana Kuka  ta Yar da kofin dake hannunta shiko yakama yimata nasiha cewa:

Malam Nomau:
 " Ladidi Kiji tsoron Allah ki kasance mai addu'a a duk inda kike." Tana kuka tana firgecewa.

Malam Nomau: 

  Sai yace: "takiramasa Dan uwansa" nan ta tashi ta rugo da gudu,babarta  tana mata magana amma tayi gaba ta garzaya ta kirashi. 

Nan da nan mahaifiyar Ladidi ta shiga gun nasa itama ta ganshi ba yadda yake.

Malam Idi Yazo da sauri shi da Ladidi, ya durkusa gabansa, nan M Nomau yabashi amanar iyalinsa da Kuma dukiyarsa.

Malam Nomau:
Ya rike hannun dan uwansa Malam Idi yace:

"Kaji tsoron Allah ga iyalina da dukiyata ka kulammin dasu wasu abubuwa nawa ba sai nafadama ka sansu."

nan take ya mutu.  Suka kama kuka shiko Malam  Idi yatashi ya futa da alamar murna a fuskarsa, sukuma sunata kuka. 

 Malam Idi ya hana zaman makoki:

  Ya hana Zaman makoki ya samu abokin Malam Nomau wato Soja kan batun dawo da kadarori da suke a gunsa, Soja yayi mamakin wannan lamari.

Malam Idi:

Yahadu da soja a hanya bayanda soja yadawo daga wata tafiya sai Malam idi yace:

"Yauwa daman kai nake nema domin ka dawomin da gonaki dake hannunka na dan uwana Nomau."
 
Soja:

"Yo mai yafaru kake wannan tambaya haka ai gidan na Malam nomau zani."

Idi yace:

"Ai Malam Nomau ya mutu." Soja ya dafa kirji ya zaro ido:
"Yamutu Allah ya jikansa yai masa rahama yasa yahuta."

 Soja yace ya kara da cewa :

 To!, "zan kawo." ya tafi abinsa. Ashe shima gafiyane tsira dana bakinki. 

Gonaki dake gurinsa so yake ya cinyesu, shikenan suka shiga takun saka tsakanin Soja da M Idi kowa Yana ganin kowa macuci oh, Allah sarki Ladidi macuta sun kewayeta.tanata fama dasu.

 Ga Kuma dansa Dogo wato da Ga M Idi Shima yabi sahun ubansa wajen muzgunawa Ladidi. 

Haka ta rayu har saida uwar itama ta rasu kaka kara kaka ya ya Ladidi zata kasance a chikin wannan hali na kuncin rayuwa.

 Haka  wani lokaci taje neman taimako har gidan Malam Idi, amma  M Idi  ya koreta  yai mata fata- fata  har  matarsa  tana taremata  amma yarufeta  da fada, tayi  shiru  abinta  ta zuba ido.  

Dansa wato  Dogo  shi kuma ya biyewa  ubansa aka cigaba da  wulakanta Ladidi.

           
                 Dogo da Magatakarda 

  Dogo da abokinsa wanda shi kuma yake zuga Dogo don su chimma burinsu shi da Babansa domin ganin an mallake wa Ladidi kudinta da gonaki, shanu, gidaje,da sauransu ko tsoro basa ji.

 Ga ukuba da Allah ya tanada saboda Allah yai hani da haka akwai azaba da ya tanada ga mai cin hakkin marayu kuma tun daga Duniya zai fara fuskantar matsala.

 Sudai su Dogo da abokinsa, magatakarda da mahaifinsa ko ajikinsu,wai an yakushi kakkausa suka ci gaba da muzgunawa Ladidi duk fa don taji wahala ta sadudu. 

Ko kuma ta mutu gabaya a huta bisa zugar Maga takarda abokin sa. 

 Malam Idi ya hada kai da me Gari:

 Shikuma M Idi  yayiwa mai gari alkawarin bashi gona daga cikin gonakin Ladidi a zuwan toshiyar baki don ya bashi hadin kai komai yatafi yanda suka tsara.

Haka kuwa mai gari ya bashi hadin kai shima ya samu nasa Rabon. Kajifa uban kasa dashi aka hada kai a cinyewa marainiya hakkinta, wanda shi ya kamata a kaiwa karar andanne hakki ya kwato wai kuma shine zai cinye kaji shi kuma irin nasa salon na mugunta

 Mahaukaci da ga mai Gari:

 Gefe daya kuma mai Gari yana da wani da shi kuma mahaukacine in yaga galala sai yabika da duka haka ake ta fama da shi acikin garin ,amma idan kace dashi "in anbi Rabbana sai yace ba wahala nawa" 

Sai ya kyaleka katafi ba abinda zai maka,shikuma kaji nasa salon na mahaukata. Ku kasance damu dai cikin wannan kaya taccen shiri namu na YarMalam

Sai kuma labarin Sani, wanda shi kuma yake temakon Ladidi tunda yazo wucewa ta unguwarsu yaga dogo ya nema yayi mata wula kanci nan ya samu ya temaketa .

Shi kuma kaji yadda akai ya shigo rayuwar Ladidi yaba babansa labarin ta ,shi kuma uban yace lallai ya samu ya temaketa domin yasan zai iya.

Sai kuma kawa wadda take shareware Ladidi hawaye lokavin da ta shiga wani yanayi na ukuba da wulakanci.

Sai kubiyomu a tashar tamu wato nishadisport, a manhajar youtube. Shin waye zai nasara a wannan lamari mai rikitarwa aai kubiyomu.

In kun shiga shafin youtube kuka rubuta "nishadisport" tasharmu zata bayyana saika kalli duk wanda kake so daga shirye shiryenmu na zamani, suna da kyau ga ilmantarwa, ga Nishadantarwa gami da ban dariya maganin hawan jini.

Ankasa wannan shiri gida gida a kwai (play last) na kowane season daga (season )1 har zuwa (season ) 2 mun gode!.

         
               Wannan shine logon tashar 

   By Sadikyusuf:

   Http://nishadisport.blogspot.com.  
a tuntubemu ta wannan adireshi, sadiku854@gmail.com 
    

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Rigima ta barke ...

Labaran Mako

An tarewa Sani hanya