YAR MALAM SEASON 1 EPISODE 1 review

     Shirin Yar Malam Kashi na daya, shirine  da yake nuna rashin  rike  amana  na wani mutum da dan uwansa ya mutu  ya  bar masa dukiya ,kamar  irinsu   gonaki  dabbobi,   da  kuma kudi,  da  gidaje ,  kuma  mutimin   mai  suna  M Nomau,  mutumin  kirkine  ya  temaki  dan uwan nasa  amma  yaci  amanarsa  ga kadan  daga cikin  episode   one.  


   Ladidi na zaune a kusa da mahaifiyarta ta tashi don ta kaiwa babanta ruwa sai tasameshi a kwance ya kasa tashi, Sai nan danan ta durkusa gabansa tana Kuka  ta Yar da kofin dake hannunta shiko yakama yimata nasiha cewa taji tsoron Allah.


      Saiyace takiramasa Dan uwansa nan ta tashi ta ruga babarta  tana mata magana amma tayi gaba ta garzaya ta kirashi yazo da sauri ya durkusa gabansa, nan M Nomau yabashi amanar iyalinsa da Kuma dukiyarsa nan take ya mutu suka kama kuka shiko Malam  Idi yatashi ya futa da alamar murna a fuskarsa, sukuma sunata kuka. 


     Ya hana Zaman makoki ya samu abokin Malam Nomau wato Soja kan batun dawo da kadarori da suke a gunsa, Soja yayi mamakin wannan lamari yace to zai kawo ya tafi abinsa.Ashe shima gafiyane tsira dana bakinki gonaki dake gurinsa so take ya cinyesu shikenan suka shiga takun saka tsakanin Soja da M Idi kowa Yana ganin kowa macuci oh, Allah sarki Ladidi macuta sun kewayeta.tanata famadasu.Ga Kuma dansa Dogo wato da Ga M Idi Shima yabi sahun ubansa wajen muzgunawa Ladidi.haka ta rayu har saida uwar itama ta rasu kaka kara kaka ya ya Ladidi zata kasance a chikin wannan hali na kuncin rayuwa,  haka  wani lokaci taje neman taimako amma  M Idi  ya koreta  yai mata fata fata  har  matarsa  tana taremata  amma yarufeta  da fada, tayi  shiru  abinta  ta zuba ido,  dansa wato  Dogo  shi kuma ya biyewa  ubansa aka cigaba da  wulakanta Ladidi.

           Dogo  da  Abokinsa.

  Dogo da abokinsa wanda shi kuma yake zuga Dogo don su chimma burinsu shi da Babansa domin ganin an mallake wa Ladidi kudinta da gonaki, shanu, gidaje,da sauransu ko tsoro basa ji ga ukuba daga Allah, saboda Allah yai hani da haka akwai azaba da ya tanada ga mai cin hakkin marayu kuma tun daga Duniya zai fara fuskantar matsala.

 Sudai su Dogo da abokinsa, haka da mahaifinsa ko ajikinsu,wai an yakushi kakkausa suka ci gaba da muzgunawa Ladidi duk fai don taji wahala ta sadudu.ko kuma ta mutu gabaya a huta bisa zugar Maga takarda abokin sa. Shikuma M Idi  yayiwa mai gari alkawarin bashi gona daga cikin gonakin Ladidi a zuwan toshiyar baki don ya bashi hadin kai komai yatafi yanda suka tsara 

 Gefe daya kuma mai Gari yana da wani da shi kuma mahaukacine in yaga galala dai yabika da duka haka ake ta fama da shi acikin garin ,amma idan kace dashi in anbi Rabbana sai yace ba wahala nawa ,sai ya kyaleka katafi ba abinda zai maka,shikuma kaji nasa salon na mahaukata fuka dai cikin wannan kaya taccen shiri namu na Yar Malam. 
Sai kubiyomu a tashar tamu wato nishadisport a manhajar youtube. In kun shiga shafin youtube kuka rubuta nishadisport,tasharmu zata bayyana sika kalli duk wanda kake so daga shirye shiryenmu na zamani , suna da kyau ga ilmantarwa, ga Nishadantarwa gami da ban dariya maganin hawan mini ga logon tashar
   By Sadikyusuf
   Http://nishadisport.blogspot.com.  a tuntubemu ta wannan adireshi,   sadiku854@gmail.com 
    

Comments

Popular posts from this blog

Burinsa ya cika

Nigeria a yau