Posts

Showing posts from August, 2025

Rikicin daba a kano

     GABATARWA Rikicin ‘Yan Daba a Kano, a ga ya za'a kamo bakin zaran.Daga Sadik Yusuf, Kano Nigeria Zami duba da wannan matsala da kuma wasu al'amura na yau da kullum. Dafatan za'a kasance damu. Daga Sadik Yusuf – Kano, Nigeria Tuntuba: sadiku854@gmail.com Shafinmu: nishadisport.blogspot.com Abin Da Ke Faruwa a Kano Ya kamata mu fuskanci abinda ke faruwa mu fadawa kanmu gaskiya, game da matsalar da ke addabar jihar Kano – wato rikicin 'yan daba.  Wannan matsala da take nema ta gagari Kundila  ta shafi unguwanni da dama a jihar ta kano , kamar irinsu  Dorayi, Sheka, Dala, Zage, Kofar Mata  s harada, ja'in da kuma kurnar Asabe  da dai sauran su. A bin yazama kamar annoba.Yara da basu kai shekaru 15 zuwa 18 ba suna haduwa suyi gungu suna fada a da makamai a  tsakaninsu,  suna kai hare-hare a inda suke so.  Suna amfani da makamai masu hadari irin su adda, barandami, fafalo , da kuma kayan maye da suke shaye-shaye. Sau da dama. ...

LABARAN MAKO

Image
  GABATARWA  Salamu alaikum barkanmu da sake saduwa a wannan shafi namu mai kawo muku labarai, da al'amura na yau da kullum, wato nishadisport nine naku Sadik Yusuf har kullum da  fatan kuna lafiya. Kwamishina ya aje mukaminsa  Ga sharhin labaran dallah-dallah. Kwamishinan sufiri na jihar kano Ibrahim Namadi, ya ajiye mukaminsa na kwamishina bisa radin kansa acewarsa.inda yake cewa:  "na aje mikamina na kwamishinan sufiri, saboda na kare kima, da martabar Gwamnatin jiha kar kashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf, saboda abin da yafaru dan gane da belin wanda ake tuhuma da aikata lefin safarar miyagun kwayoyi.  "hakan ta farune saboda banyi cikakken bincikeba, na karbe shi saboda haka na ga ya dace da nayi murabus, kuma na bawa al'ummar jihar kano hakuri  da gwammnati, da yan jam"iya bisa abinda yafaru."  "Ina mika godiyata ga gwamna, saboda damar da yabani ta hidimtawa al'ummar jihar kano na gode." Kuma ya kara da cewa "na yi farinciki ...