Shekara 1 da Tinibu talaka ya koka
π° Rahoton Musamman: Shekara Daya da Bola Tinubu – Talakawa na Cikin yanayi!
Assalamu Alaikum Jama'a, da fatan kun wayi gari lafiya. Kuna tare da ni, Sadik Yusuf, a dandali na NishadiSport.
GABATARWA
A yau muna dauke da rahoto na musamman, game da halin da Najeriya ke ciki, shekara guda bayan hawan shugaba Bola Ahmed Tinubu kan karagar mulki.
⚠️ Halin Talauci da Tsadar Rayuwa
Ana bikin cikar gwammnatin A P C hawa karagar mulkin Nigeria shekar biyu. A cewar jama’a da dama, ba’a gani ba, a kasa sai dai ana ji a jiki– babu wani cigaba da talaka zai iya nunawa, cewa gashi yasamu sauki a wannan gwamnati.
Ana cikin ma wuyacin hali a wannan lokaci na mulkin farar Hula, abin ba'a cewa komai sai dai neman sauki a wannan kasa Nigeria.
Ga wasu daga cikin manyan matsalolin da suka dabaibaye rayuwar yau:
- π Rashin wutar lantarki
- π§ Rashin ruwan sha
- π Ilimi ya tabarbare
- π« Rashin tsaro – ana kisa kullum, ana ji, ana gani
- π Tsadar abinci – hatta biredi ya gagari talaka
- πΎ Wake ana aunawa kwano – Naira 4,000!
- π₯ Lafiya? Komai sai mutum yayi da kansa
- π Shinkafar gida (mudu) – Naira 3,800!
A irin wannan yanayi, jama’a da dama sun shiga halin kaka-nika-yi, inda ake tambayar cewa to ina talaka zai sa kansa? Lamarin rayuwa daga wannan sai wannan, yau kaji ance an cire tallafin mai, sai kuma kaji ance an cire na wuta ko kuma na asibiti, wanda manufofin shugaba Bola Ahamad Tinubu sun jefa al'ummar Nigeria cikin halin ni 'ya su.
Mutane suna mutuwa saboda basu da kudin magani a asibiti,ko abin da zasu sa a bakinsu, wasu sai sunyi roko, kana suke samu,wasu kuma su cinye dan jarin da suke dashi sai su dawo su tsuguna.
Ana fatan ganin samun sauki a wannan yanayi na kunci, gwamnati ta san yanda zatai don ganin al'umma sun samu sauki, muna fatan gani haka.
πͺ Sojoji Sun Fara Taka Tsantsan
A rahotonmu na musamman, sojoji sun bayyana cewa ba za su lamunci kisan da ake yi wa ‘yan uwansu ba.
Domin ana bi har barikinsu akashesu, a dauke makamansu sunaji suna gani. Wannan daliline yasa babban hafsan sokin ya magantu.
Cewa bazasu laminci wannan lamariba, na kisan 'yan uwansu, yakamata sojoji su farka su san abinda sukeyi su kula da kansu, wanda sune alhakin kare kasa da 'yankasa ya rataya a wuyansu to suma ana musu kisan mummuke yo ina kuma ga talakawa.
yakamata gwamnati ta samar da yanayi mai kyau na sabunta harkar tsaro a Nigeria, a samar da kayan aiki na zamani hakan zai taimaka wajen kawo karshen wannan lamari.
To abun jira a gani – shin sojojin za su dauki mataki ko kuma zance ne kawai?
Allah ya kyauta.
π Tsadar Sallah Babba – Shanu da Raguna Sun Zama masu tsada πͺ
Yayin da Sallah Babba ke tafe, tsadar dabbobin layya na kara kamari:
- Shanu da raguna suna kara tsada kowace rana.
- Jama’a da dama suna kasa sayen dabba saboda matsin tattalin arziki.
- Ana ganin hakan ya samo asaline saboda shugaban kasar Niger Muhammadu chani, ya hana futa da dabbobi daga kassr tasa, domin shima 'yan kasarsa su samu sauki.
- Sukuma 'yan Nigeria suna ganin wannan matakine ya haifar da wannan mummunan tsadar dabbar, saboda kusan duk Shanun daga kasar ta Niger ne ake shigowa dasu Nigeria.
Mungana da wani mazaunin birnin Kano (wanda ya bukaci a boye sunansa), ya bayyana cewa:
"Ai tsadar abinci ta fi komai a yanzu. Babu maganar sayen dabba, kawai dai idan anyi hadin gwiwa ana samun nama."
Wasu mutane suna hada kudi – mutum 7 ko fiye – domin sayen dabba guda, domin yin layya cikin hadin kai, yayin da wasu kuma kawai suke sayen nama domin su dandana daga cikin albarkar Sallah.
kuma iyali suma suce sunyi laiyya mutane sukance a maida mugun yawu, ko kuma kar yara su shiga makwafta suga ana suya, sukuma ba'ayi a gidansu.
wasu kuma sukance kafi zuru. Allah ya kawo sauki.
< Tsokaci Sallah ta wuce ta bar wawa da bashi.π
Hausawa su kance! Sallah tawuce ta bar wawa da bashi. Hakan yasamo saline saboda musulunci bai ce lallai sai mutum yayi layyaba.
layya Sunnace, ba farillah ba, amma dai sunnah ce mai karfi gamasu hali suyi duk shekara ta babbar Sallah, wanda bashi da hali ba'a ce lallai sai yayiba don haka ba'a ce mutum yaci bashiba domin yin layya.
Manzon tsaira annabin rahama, ya yi layya da manyan Raguna guda biyu, yace daya nawa, daya kuma na al'umma ta. Ga wanda bai yiba.
Yo kaga kar ka takurawa kanka wajen. Cewa lallai sai ka yi layya musulinci yana da sauki da afuwa Allah ya hore mana abin yin layya amin.
In kuma mutane zasuyi hadaka in sane akace mutum bakwai, in Rakumine mutum goma, hakan in akayi shima akwai ladan layya, wannan ma saukine ga marasa hali.
<Halin mutane na boye nama
Wani lamari kuma na halayyar mutane. wanda suka samu sukayi layya shine, rowa da kuma boye nama.
Allah subhanahu wata' ala ya umarci mutane cewa in sunyi layya, to su kasa naman guda uku, daya suci, daya kuma su bayar, daya su aje shi.
To amma sai kaga ba'a yin hakan, dan kadan ake ba mutane wani lokacin kuma abaka mara kyau, wanda ba'a so, so hanji ko kitse, har ma da kashi, mutane sukan aje nama har tsawon shekara guda, wata Sallah ta tarar da wata.
Kuma naman har rubewa yake, yayi ta yin funfuna, amma bazasu ciba baza su bayarba, ko mai zasuyi dashi? Oho!.
yakamata mutane su rika bayar da nama fi sabilillahi, domin abin da ka bayar shi zaka tarar, wanda kuwa kaci, kashi zai zama, wanima ya zamema cuta, don haka mu kiyaye. Allah ya hore.
π§Ύ Kammalawa
Halin da ake ciki a Najeriya yanzu na bukatar addu'a, hakuri, da kokari daga kowa da kowa.
Gwamnati na da alhakin saukaka rayuwar talaka, amma har yanzu jama’a na fama da matsaloli kala-kala.
Kama da rashin mahalli,rashin abinci,ga kuma lafiya. Wa 'yan nan kullum zaka ga mutane sunabi kwararo-kwararo suna neman a temakamusu.
Musamman 'yan gudun hijira da masifar 'yan Bindiga ta shafa da kuma rikin Boko Haram na arewa maso gabas wannan mutane suna bukatar taimako daga gwamnati.
Suma irin wannan mutanen suna zuwa makwaftan jihohinsu, suyi ta roko suna neman abin sawa a bakin salati. Allah ya kawo saukin lamura a Nigeria don samun saukin mabarata amin.bbchausa
Muna rokon Allah Ya kawo sauki, ya ba mu zaman lafiya da saukin rayuwa. Amin. Sai a saurari labarai na gaba a wannan shafi namu na blogs nishadisport.
Mawallafi: Sadik Yusuf
π nishadisport.blogspot.com
π§ sadiku854@gmail.com
Comments
Post a Comment