Takaddamar karancin albashi a nig

   Har yanzu tana kasa tana dabo batun mafi karancin albashi a Nigeria inda ake dakon shuganba kasa Bola Ahamad Tinibu, da ya fitar da sanarwa ta karshe,a bikin ranar dmokradiya na sha biyu Ga watan yuni a eggle square a birnin tarayya dake Abuja, inda a Wannan wajene ya sanar da mafi karancin albashi na naira dubu sittin da biyu  saboda yayi la'akari da matsin tattalin arziki da ake fama a kasar, su Kuma anasu bangaren Yan kwadago sunyi watsi da naira dubu sittin da biyu inda suke fafutuka akan abasu naira dubu Dari biyu da hamsin, inda ita Kuma anata bangaren gwammnatin tarayya take ganin ba zaiyiwuba maganin bari Kar asoma .


   Sukuma talakawa Suna ganin Yan kwadago suyi fafutikar ganin ansaukaka farashin kayayyaki a kasar memakon batun Karin albashi saboda inma ankara albashin zaitafine a sayen kayayyaki saboda tabbas ana Karin albashi kaya Kuma zasu tashi kaga anyi ba aiba Kenan , al'adar kasa Nigeria indai za ai karin albashi to kuwa la shakka kaya sai sun tashi to gana anbaka da dama an karbe da hagu za'a koma yar gidan jiyane shi yasa yafi dacewa asamu kaya su sauka kawai in yaso a hakura da kari albashi.  Inji wasu yangari, na zanta da wani mazaunin birnin Kano, inda yabukaci da in boye sunansa,yake shaida min cewa gara a rage farashin kaya komai ya sakko shi yafi da ai karin albashi, wani mai suna Malam Ibrahim shikuma yace gara a sakko da farashin dala kaya su sakko shi yafi da karin albashin , saboda in kaya na tsada an karawa ma'aikata kudi yo sukuma ragiwar talakawan gari ya za suyi gwanda ma ma'aikata kenan. Shikuma wani karamin ma'aikaci cewa yayi baya goyon bayan karin albashi shima ,yace so yake kaya suyi sauki domin mafi karancin albashi na naira dubu sittin da biyu  ba zai ishi karamin ma'aikaciba domin shinkafa kwano yakai dubu biyar , mai dubu biyu da dari biyar ga kudin transport, ga kudin makarantar yara ,rashin lafiya kuma karshe ga iya yenka suma suna jira to ina mutum zai sa kansa. Karshe yayi addu'ar Allah ya kawo dauki.



   A wani bangare kuma ana cigaba da ganin fitaccen attajiri na Africa Baki daya wato, Aliko Dan Gote, Yana kokarin ganin ya fara Sai da manfetur a Nigeria Amma Kuma Yana zargin anai masa kafar ungulu wajen ganin ya fara sakin man Wanda ana ganin in yafara Sai da man na fetur to zai sakko man ana tinanin litar man zata koma naira Dari biyar da hamsin, shi isa suke masa dingushe sun hana shi danyen mai duk da cewa akasar ake hako man ,domin manyan basa so arika tace mai a kasar domin suna samun riba sosai wajen shigo da ta taccen man fetir,suna ganin in har Dan Gote yafara tace mai yo su sunrasa samun wannan kudi .

 

 Anasu bangaren suna ganin gwamnati bata kyautaba da za'a hana matatar mai ta Dan Gote domin suna ganin in yafara to mai zai sakko asamu saukin rawa kowa ya samu sassauci kaya su sakko, mu samman abinci wanda shi yafi damun mutane, ci uku ya gagari mutane in mutum yasu yaci abinci sau daya to ya dace ubangiji Allah ya kawowa talakan Nigeria dauki domi in mutum yana da yara kamar biyar tofa in baya samun naira dubu goma to akwai matsala domin yana cikin matsala. 


 Daga Sadik Yusuf

  nishadisport.blogspot.com

Comments

Popular posts from this blog

YAR MALAM SEASON 1 EPISODE 1 review

Burinsa ya cika

Nigeria a yau