LADIDI TA SHIGA TASKU

      Tofa ana cikin tufka da warwara mama mahaifiyar Ladidi kuma takama rashin lafiya,, gaba kura baya Siyaki, ga basu da kudi ko ruwan sha Babu agidan nasu haka Ladidi ta fita neman tai mako tahadu da Dan gurgu, Yana mata magana amma ta manta dashi taki kulashi ya dauki kudi ya bata amma taki karba wai ita bata sonsa, haka ta tafi tabarshi da zaton wanine yake huremata kunne yayi kwafa yace zasu gamu. Wani lamari sai rashin kauna ace mutum Yana ciki matsala abashi kudi yaki karba to allh ya sawake.

      Shiko Sani har yanzu Yana Fadi tashin ganin gidan su Ladidi bisa umarnin mahaifinsa wato Malam da kuma te makon mahaifiyarsa duk Wanda ya tambaya sai ace ba'asaniba sai ya gaji ya koma gida. Sukuma su Dogo suna ta faman ya zasuyi suzubar da cikin da man Ladidi take dashi suke,amma abin yaci tura saboda sun dogara ga Allah kuma Allah Yana tai makonsu har rannan da kansa Dogo yaje gidan su Ladidi Dan Tasha maganin da yakaimata na zubar da cikin amma da taimakon Ladidi maga ni ya zube da kwallah kara magani ya zube haka Ladidi tayi murna kuma mama ta yadda da abin da Ladidi take fadamata na kar ta yadda da su Dogo,shikuma haka yafita da borin kunya ya bar gidan maga takarda na masa magana amma yaki saurarensa.

    Amma duk da haka Dogo bai hakuraba Maga takarda yacigaba da ziga Dogo sunata kitsa yadda zasu zubar da cikin mama mahaifiyar Ladidi amma Allah Yana karesu Suna tsallakewa domin sun dogara Ga Allah tabaraka wata ala ,domin duk Wanda ya dogara Ga Allah ,Allah ya isar masa akokarin Dogo  na ganin ya zubar da cikin Mama ma haifiyar Ladidi  ya je ya samo wani magani ya kaiwa inna ma haifiyarsa don taje ta kaiwa Mama ko tafi yadda da ita saboda su bazata amince da suba,  yaje kamar mutimin kirki ya ba inna itako taki karba ta zubar ta koreshi ya tashi ba nauyi yaje yagayawa Magatakarda, kamar yadda ya saba yadorashi kan cewa yanzu yaje da kansa yayi yan dabaru yabata ta tasha a gabansa yako amince yatafi .
  Yayi sallama ta amsa tayi mamakin ganinsa a wannan lokaci saboda tun rasuwar mijinta baizo gidanba sai yanzu ashe yazo zalincine,mun godewa Allah.
  Wanda ya wallafa, Sadikyusuf
      @nishadisport

Comments

Popular posts from this blog

YAR MALAM SEASON 1 EPISODE 1 review

Burinsa ya cika

Nigeria a yau